Home » Ƙasar Nijar: Ana Cigaba da Samun Safarar Ƙwayoyi daga Najeriya

Ƙasar Nijar: Ana Cigaba da Samun Safarar Ƙwayoyi daga Najeriya

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Hukumomi a Jamhuriyar Nijar sun bayyana damuwarsu kan ƙaruwar fasa-ƙwaurin miyagun ƙwayoyi a tsakanin iyakokin ƙasarta da Najeriya da kuma Jamhuriyar Benin.

Hakan na zuwa ne bayan da aka kama ɗaruruwan ɗaurin tabar wiwi da wata ƙwaya nau’in baliyam mai hatsari, da aka yi yunƙurin shigar da su ƙasar a ranar Juma’a daga wata ƙasa mai maƙwabtaka da su.

Shugaban gundumar Gaya a cikin jihar Dosso, da ke Kudu Maso Yammacin Nijar, Ashimu Abarshi, ne ya yi wa manema labarai ƙarin bayani game da kama miyagun ƙwayoyi da ka yi.

Ya ce ƙwayoyin da suka kama sun haɗa da tabar wiwi ɗauri 400 da kuma ɗauri 1,260 na wata ƙwaya mai suna Diezepam, da ɗauri biyar na ganyen wiwi, da aka yiwo fasa-ƙwaurinsu a cikin kwale-kwale ta Kogin Isa.

Jami’in ya ce a baya-bayan nan, sun lura masu fasa-ƙwaurin ƙwayoyi na ƙara ƙaimi wajen safarar miyagun ƙwayoyi ta cikin Jamhuriyar Nijar.

Ashimu Abarshi bai bayyana ƙasar da suke zargin ake shirin shiga da ƙwayoyin ba daga Nijar, amma ya tabbatar da cewa ƙwayoyin sun fito ne daga Jamhuriyar Benin da Nijar da kuma Najeriya.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?