• Home  
  • Kwara: Wani Alƙalin Alƙalai Ya Riga Mu Gidan Gaskiya
- Labarai

Kwara: Wani Alƙalin Alƙalai Ya Riga Mu Gidan Gaskiya

Allah ya yi wa Tsohon alƙalin alƙalan kotun ɗaukaka ƙara ta shari’ar musulunci ta jihar Kwara rasuwa, mai shari’a Abdulmutallib Ahmad Ambali.

Allah ya yi wa Tsohon alƙalin alƙalan kotun ɗaukaka ƙara ta shari’ar musulunci ta jihar Kwara rasuwa, mai shari’a Abdulmutallib Ahmad Ambali.

Marigayin ya rasu ne a safiyar yau Alhamis a asibitin koyarwa na jami’ar Ilorin (UITH), Oke-Oyi, bayan ƴar gajeruwar rashin lafiya.  Ya rasu yana da shekara 83 a duniya. 

Marigayin shine alƙalin alƙalai na biyu bayan mai shari’a Abdulkadir Orire, kuma rajistara na farko a kotun ɗaukaka ƙara ta shari’ar musulunci a jihar Kwara.

Marigayi Abdulmutallib Ahmad Ambali ya kwashe shekara 8 a kujerar alƙalin alƙalan daga shekarar 2001 zuwa 2008.

A wata tattauna ta manema labarai, alƙalin alƙalan musulunci na jihar Kwara, mai shari’a Abdullateef Kamaldeen wanda ya tabbatar da rasuwar, ya bayyana marigayin a matsayin mutum mai tsoron Allah, haziƙin alƙali wanda yayi riƙo da koyarwar addinin musulunci.

Ya bayyana marigayin a matsayin mutumin kirkiri, mai riƙo da addini, mai kyawawan halaye wanda baya raina kowa.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai