• Home  
  • Dangote Ya Gode Wa Buhari Bisa Karfafa Masa Guiwa Wajen Kai Wa Ga Gaci
- Labarai

Dangote Ya Gode Wa Buhari Bisa Karfafa Masa Guiwa Wajen Kai Wa Ga Gaci

A cigaba da bikin ƙaddamar da kanfanin na Dangote, shugaban gamayyar kanfanin Dangote, Aliko Dangote, ya gode wa shugaba Buhari bisa ƙarfafa masa guiw

Aliko Dangote Ya Gode Wa Buhari Bisa Karfafa Masa Guiwa Wajen Kai Wa Ga Gaci

A cigaba da bikin ƙaddamar da kanfanin na Dangote, shugaban gamayyar kanfanin Dangote, Aliko Dangote, ya gode wa shugaba Buhari bisa ƙarfafa masa guiwa wajen kai wa ga kammala kafa matatar man fetur irinta ta farko a Afirka.

Dangote ya bayyana hakan ne a yayin bikin ƙaddamar da aikin kammala kanfanin Tace Man da aka yi yau a jihar legas.

Inda ya bayyana cewa ya fara wannan yunƙurin kafa wannan kanfani ne a ‘yan shekarun baya, sai dai ya yi ta gamuwa da matsaloli masu yawan gaske.

Sai dai a yanzu ya yi matuƙar farin ciki bayan da mafarkinsa ya zama gaskiya.

Sannan Dangote ya gode wa gwamnatin jihar legas tun daga tsohon gwamnan jihar Bola Tinubu wanda ya jagoranci jihar daga shekarar 1999 zuwa 2007 zuwa ga gwmna mai ci Babajide Sanwo-Olu bisa gudunmuwar da suka ba shi.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai