• Home  
  • Allah Ya Yi Wa Rajistaran Jami’ar Bayero Rasuwa
- Labarai

Allah Ya Yi Wa Rajistaran Jami’ar Bayero Rasuwa

Wannan sanarwa wannan rashi da jami’ar Bayero ta yi, ya fito ne daga hannun Daraktan Hulɗa da Jama’a na Jami’ar Bayero Kano, Malam Lamara Garba.

Wannan sanarwa wannan rashi da jami’ar Bayero ta yi, ya fito ne daga hannun Daraktan Hulɗa da Jama’a na Jami’ar Bayero Kano, Malam Lamara Garba.

Ya bayyana cewa Rajistaran ya rasu da sanyin safiya ranar Laraban nan.

Inda aka gudanar da sallar jana’iza da ƙarfe goma 10:00 na safe a babban masallacin dake sabon reshen jam’iyyar ta Bayero.

Malam Jamilu Ahmed Salim, ya shafe tsawon shekaru huɗu a matsayin rajistaran Jami’ar kuma Malam Lamara ya bayyana shi a matsayin haziƙi wanda ya ba da gudunmuwa mai yawan gaske ga cigaban jami’ar.

Sannan ya yi addu’ar Allah ya gafarta masa tare da saka masa da gidan Aljanna.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai