• Home  
  • Ana Cigaba da Samun Ƙarin Hukuncin Kisa a Ƙasar Iran
- Kasashen Ketare - Labarai

Ana Cigaba da Samun Ƙarin Hukuncin Kisa a Ƙasar Iran

Hukumar kare hakkin bil adama ta Majalisar Dinkin Duniya ta yi Alla-wadai da karuwar hukuncin kisa a ƙasar Iran, ciki har da wadanda ke da hannu a zanga-zangar kasar.

Hukumar kare hakkin bil adama ta Majalisar Dinkin Duniya ta yi Alla-wadai da karuwar hukuncin kisa a ƙasar Iran, ciki har da wadanda ke da hannu a zanga-zangar kasar.

Hukumar ta amince da wani Ƙuduri da ke nuna matukar damuwa kan yadda ake samun karuwar mutanen da ake kashewa ta wannan hanya, ciki har da mutanen da aka yanke wa hukuncin kisa saboda zargin su da hannu a zanga-zangar baya-bayan nan.

Kudirin wanda ya kara wa’adin mai ba da rahoto na musamman na Majalisar Dinkin Duniya kan harkokin kare hakkin bil adama a Iran da tsawon shekara guda, ya samu kuri’un amincewa 23 daga cikin wakilan hukumar 47.

Wasu wakilai 6 sun kaurace wa kada kuri’ar, a yayin da ƘASAR China da Cuba da Pakistan da Vietnam suka kasance cikin kasashe 8 da suka yi adawa da wannan mataki.

Kudurin ya yi nuni da kakkausar suka daga kasashen duniya kan murkushe masu zanga-zangar da kasar ta Iran ta yi a watan Satumban bara.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000