Home » Bangarorin da ke yaki a Sudan sun yi fatali da yarjejeniyar tsagaita wuta na bikin sallah

Bangarorin da ke yaki a Sudan sun yi fatali da yarjejeniyar tsagaita wuta na bikin sallah

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Bangarorin da ke yaki a Sudan sun yi fatali da yarjejeniyar zagaita wuta na bikin sallah

Da alama yarjejeniyar tsagaita wuta da aka ayyana tsakanin ɓangarorin mayaƙa biyu da ke gumurzu da juna a Sudan, domin bikin Idin babbar sallah, ta ruguje.

Wata mai aikin agaji, Duaa Tariq ta shaida wa manema labarai cewa an rinƙa jin rugugin manyan bidigogi a wasu sassa na Khartoum, babban birnin ƙasar tun da sanyin safiyar yau.

A ranar Talata ne, shugaban gwamnatin mulkin sojin Sudan, Abdel Fattah al-Burhan ya yi kira ga matasa da su shiga yaƙin da ake yi da mayaƙan RSF.

Sai dai Tariq ta shaida wa manema labarai cewar dakarun RSF ɗin ne suka fi yawa a Khartoum, inda suka mamaye gidaje da kasuwanni da kuma titunan birnin.

Wasu yarjeniyoyin da aka cimma a baya duk sun gamu da naƙasu wanda hakan ya haifar da cigaba da gwabza faɗa da ake yi.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?