Home » Cire Tallafin Mai: Majalisar tattalin arzikin Najeriya ta ba da shawarar ba da tallafi ga al’umma

Cire Tallafin Mai: Majalisar tattalin arzikin Najeriya ta ba da shawarar ba da tallafi ga al’umma

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Majalisar Tattalin Arzikin Najeriya NEC ta ba da shawarar a bayar da tallafi ga ma’aikata da marasa galihu don rage raɗaɗin cire tallafin mai a ƙasar nan.

Majalisar Tattalin Arzikin Najeriya NEC ta ba da shawarar a bayar da tallafi ga ma’aikata da marasa galihu don rage raɗaɗin cire tallafin mai a ƙasar nan.

Gwamnan jihar Bauchi Bala Mohammed ne ya bayyana haka ga manema labarai jim kaɗan bayan kammala taron ƙaddamar da majalisar wadda mataimakin shugaban ƙasa Sanata Kashim Shettima ke jagoranta.

Majalisar ta bayar da shawarar ne bayan da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya umarce ta da ɓullo da hanyoyin rage raɗadin.

Gwamnan ya ce majalisar ta yi la’akari da shawarwarin da Hukumar Kula da Albashi da Ma’aikata ta Kasa ta bayar na biyan Naira biliyan 702 a matsayin alawus-alawus na rayuwa ga ma’aikatan gwamnati a wani ɓangare na rage raɗadin.

A lokacin taron majalisar, an kafa wani kwamiti da zai gudanar da aiki, cikin makonni biyu, don yin nazarin hanyoyin da za a bi wajen raba kayan agajin.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?