Home » Dan Majalisa Ya Gwangaje ‘Yarsa Da Kyautar Mota Bayan Kammala Sakandire

Dan Majalisa Ya Gwangaje ‘Yarsa Da Kyautar Mota Bayan Kammala Sakandire

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

‘Dan majalisa mai wakiltar mazabar Pankshin da Kanke da Kanam a  majalisar tarayya daga jihar Filato Yusuf Gagdi, ya gwangwaje ‘yarsa Aisha da sabuwar motar alfarma ta gani da fada. 

Gagdi ya sayawa diyar motar ne domin murnar kammala karatun makarantar sakandire da kuma samun maki mai kyau a jarrabawar sharar fagen shiga jami’a JAMB

Aisha Gagdi ta kammala karatunta a makarantar Lead British International School Abuja a ranar Asabar.

Wani ma’abocin Facebook, Saminu Maigoro ne ya wallafa hotunan yarinyar da mahaifinta a cikin motar. 

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?