Home » Gamnatin Jihar Kano Ta Janye Dokar Hana Zirga-zirgar Ababen Hawa

Gamnatin Jihar Kano Ta Janye Dokar Hana Zirga-zirgar Ababen Hawa

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Gwamantin Jihar Kano ta sanar da janye dokar hana zirga-zirga da ta sanya a safiyar jiya Litinin bayan sanar da sakamakon zaben gwamna da na ’yan majalisar jihar.

Gwamnatin Kanon ta sanya dokar hana fita ne a jihar da nufin kauce wa tabarbarewar doka da oda biyo bayan bayyana sakamakon zaben gwamna da na ‘yan majalisar dokokin jihar.

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida na Kano, Muhammad Garba, shi ya sanar da dage dokar a cikin wata sanarwa da ya fitar a daren jiya.

Ya ce gwamnatin ta dage dokar  bayan ta yi nazari sosai kan lamarin da kuma kwanciyar hankali da ya wanzu a fadin jihar.

Kwamishinan ya yi kira ga bankunan kasuwanci da ma’aikatan gwamnati da sauran al’ummar jihar da su fito su ci gaba da sana’o’insu na yau da kullum.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?