Home » Gombe: Jam’iyyar APC ta Dakatar da Sanata Amos Bulus Bisa Wani Zargi

Gombe: Jam’iyyar APC ta Dakatar da Sanata Amos Bulus Bisa Wani Zargi

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da , sakataren yada labaran jam’iyyar APC na jihar MOSES KYARI, ya sanyawa hannu ranar Asabar a Gombe.

Kyari ya ce jam’iyyar ta kuma dakatar da dan majalisar wakilai Yunusa Abubakar mai wakiltar mazabar Yamaltu-Deba a majalisar dokokin tarayya bisa zargin yi wa jam’iyyar zagon kasa.

Ya ce shugabannin mazabarsu sun dakatar da ’yan majalisar ne bayan an same su da aikata laifukan cin hanci da rashawa a lokacin zaben 2023 a jihar.

Kyari, ya ce shugabannin Unguwar Bambam da ke karamar hukumar Balanga ne suka dakatar da Sanatan.

Kyari, ya ce an kafa kwamitin da zai binciki lamarin inda ya ce kwamitin ya gayyaci Sanatan amma bai iya kare kansa daga zargin ba don haka kwamitin ya ba da shawarar dakatar da shi daga jam’iyyar.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?