Home » Gwamnan Kano Ya Amince da Mai da Barista Muhuyi Magaji Kan Kujerarsa

Gwamnan Kano Ya Amince da Mai da Barista Muhuyi Magaji Kan Kujerarsa

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Gwamnan Kano Ya Amince da Mai da Barista Muhuyi Magaji Kan Kujerarsa

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya amince da mayar da Barista Muhuyi Magaji Rimin Gado a matsayin Shugaban Hukumar Sauraron Korafe-korafen Al’umma da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta jihar Kano, domin kammala wa’adinsa.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labaran gwamnan jihar ta Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar.

A baya dai gwamnatin da ta gabata ta Abdullahi Umar Gnaduje ta dakatar da Muhuyi tare da tsige shi daga mukaminsa bayan majalisar dokokin jiha ta ce tana da shakku kan yadda yake gudanar da ayyukansa.

Sanarwar ta bayyana cewa Barista Muhuyi zai koma kan aikinsa ne nan take.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?