Home » Gwamnatin ganduje ta miƙa muhimman bayanai ga gwamanatin Abba Gida-Gida

Gwamnatin ganduje ta miƙa muhimman bayanai ga gwamanatin Abba Gida-Gida

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Gwamnatin ganduje ta miƙa muhimman bayanai ga gwamanatin Abba Gida-Gida

Gwamnatin jihar kano ta miƙa muhimman bayanan gwamnatin ga kwamitin karɓar mulki na jam’iyyar NNPP dake karkashin jagorancin Shugaban kwamitin Dr. Abdullahi Baffa Bichi.

Shugaban kwamitin miƙa mulki na jam’iyyar APC kuma Sakataren gwamnatin jihar kano, Alhaji Usman Alhaji ne ya mika muhimman bayanan a madadin gwamnatin mai barin gado a gidan gwamnatin kano.

Usman Alhaji ya ce, sun Sami fahimta juna sosai wajen gudanar da aiki saboda dukkanin bangarorin magana suke ta yadda za’a ciyar da jihar kano gaba.

A jawabinsa Shugaban kwamitin karɓar mulki na jam’iyyar NNPP Dr. Abdullahi Baffa Bichi, ya yabawa kwamitin miƙa mulkin Saboda yadda suka gudanar da aikin tattara bayanan.

Wannan dai na daga cikin tsare-tsaren shigar sabuwar gwamnati domin kama aiki a ranar litinin mai zuwa 29 ga watan mayun da muke ciki.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?