• Home  
  • Gwamnatin Kano za ta sake gina shataletalen gidan gwamnati da ta rushe
- Labarai

Gwamnatin Kano za ta sake gina shataletalen gidan gwamnati da ta rushe

Gwamnan jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf ya bayyana kudurin sake gina katafaren shatale-talen gidan gwamnatin jihar da aka rusa a kwanakin baya a daura da gadar Naibawa.

Gwamnatin Kano za ta sake gina shataletalen gidan gwamnati da ta rushe

Gwamnan jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf ya bayyana kudurin sake gina katafaren shatale-talen gidan gwamnatin jihar da aka rusa a kwanakin baya a daura da gadar Naibawa.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana hakan ne a yayin da yake gana wa da mai zanen shatale-talen ‘Golden Jubilee Kaltume Ghana.

Ya ce bayan gudanar da cikakken bincike, wurin ya dace da zanen kuma ba zai haifar da wani kalubalen tsaro ba, ya kuma sake tabbatar wa ‘yan jihar cigaba da samar da ayyukan more rayuwa masu inganci.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000