• Home  
  • Hatsarin Kwale-Kwale Ya Yi Sanadin Rasa Rayuka A Adamawa
- Labarai

Hatsarin Kwale-Kwale Ya Yi Sanadin Rasa Rayuka A Adamawa

An tabbatar da mutuwar mutane takwas a Rugange da ke ƙaramar Hukumar Yola ta Kudu, a jihar Adamawa, sanadiyar kifewar kwale-kwale a ƙarshen makon nan, kuma  wasu mutane 15 sun ɓace a ruwa ba a gan su ba.

An tabbatar da mutuwar mutane takwas a Rugange da ke ƙaramar Hukumar Yola ta Kudu, a jihar Adamawa, sanadiyar kifewar kwale-kwale a ƙarshen makon nan, kuma  wasu mutane 15 sun ɓace a ruwa ba a gan su ba.

Kwale-kwalen na ɗauke da fasinjoji 23 a lokacin da ya kife a ruwa sanadiyar wata gagarumar iska da ta rutsa da su.

Kakakin rundunar ƴan sandan jihar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ya faɗa cewa a cikin gawarwakin mutane takwas da aka tsamo, akwai mata 6 da maza biyu. Kuma ya bayar da tabbacin cewa nan kusa zai yi ƙarin bayani kan halin da ake ciki game da hatsarin kwale-kwalen.

Wani mazaunin yankin mai suna Mahmud wanda tare da shi ake aikin ceton, ya faɗa wa manema labarai cewa mummunan hatsarin ya faru ne saboda mawuyacin halin da kwale-kwalen ya samu kansa a ciki a lokacin da iskar ta taso, kuma yace har ma da rashin yin amfani da irin ƴan rigunan nan da ake kira life jacket masu hana mutane nitsewa a ruwa.

Yace shekaru talatin ke nan yana zaune a yankin amma bai taɓa ganin mummunan hatsarin kwale-kwale irin wannan ba, sannan ya yi kira ga gwamnati ta samar wa al’ummar yankin mafita mai ɗorewa,  a cewarsa, dole ne mutane su shiga kwale-kwale don zuwa kasuwa da gudanar da sauran harkokinsu na rayuwar yau da kullum, saboda hanyar mota ɗaya da suke amfani da ita ta kwararraɓe.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai