Home » INEC Ta dage zaɓen gwamnoni da’Yan Majalisun Jihohi a Najeriya

INEC Ta dage zaɓen gwamnoni da’Yan Majalisun Jihohi a Najeriya

by Aishatu Sule
0 comment

Hukumar Zaɓe ta Najeriya INEC ta ɗage zaɓen gwamnoni da na ‘yan majalisar dokokin jihohi da mako guda, wato zuwa 18 ga watan Maris ɗin shekarar da muke ciki.

INEC ta tabbatar da hakane a wani takarda na ɗage zaɓen, bayan wani taron gaggawa da manyan jami’an hukumar suka yi a dare jiya laraba a Abuja.

Kafofin yaɗa labarai na Najeriya sun ambato cewa INEC ba ta kammala saita ‘tantance masu zaɓe ba ta BVAS wadda aka yi amfani da ita a zaɓen shugaban ƙasa a ranar 25 ga watan Fabirairu.

Sun ƙara da cewa hukumar ta ce sai ta samu damar kwashe bayananta da ta tattara na a yayin zaɓen shugaban ƙasar zuwa wani rumbunta na daban kafin ta sake saita na’urar ta yadda za a yi zaɓen gwamnoni da na ‘yan majalisar jihohi ba tare da wata damuwa ba.

Tun da farko, an tsara gudanar da zaɓen ne a ranar asabar 11 ga watan Maris.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?