Home » Kano: Kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar wa da Gawuna nasara

Kano: Kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar wa da Gawuna nasara

by Muhammad Auwal Suleiman
1 comment
Kano: Kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar wa da Gawuna nasara

Kotun ɗaukaka ƙara da ke zaman a babban birnin tarayya Abuja ta bayyana tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano, Nasiru Yusuf Gawuna kuma dan takarar APC a matsayin wanda yai nasara a zaben gwamnan jihar Kano da aka gudanar a ranar 18 ga watan maris da ya gabata. 

A hukuncin da ta yanke, Kotun ta yi watsi da ƙarar da gwamna mai ci, Abba Kabir Yusuf na jam’iyya NNPP ya ɗaukaka yana ƙalubalantar hukuncin kotun sauraron ƙorafin zaɓen ta jihar Kano.

A ranar 20 ga watan Satumba ne kotun sauraron ƙorafin zaɓe ta jihar Kano ta ce Gawuna ne ya lashe zaɓen.

Inda kotun ta  ce ba za a sanya ƙuri’u dubu 165 da dari 663 da aka kaɗa wa Abba Kabir cikin lissafi ba kasancewar babu sa hannu ko tambarin hukumar zaɓe a jikinsu.

You may also like

1 comment

Abdurrahman Abubakar November 17, 2023 - 6:55 pm

Allah yatabbatar mana da alkhairi

Reply

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?