• Home  
  • Kungiyar NLC ta sha alwashin sake tafiya yajin aiki na gargaɗi
- Labarai

Kungiyar NLC ta sha alwashin sake tafiya yajin aiki na gargaɗi

Kungiyar NLC ta sha alwashin sake tafiya yajin aiki na gargaɗi

Kungiyar NLC ta sha alwashin sake tafiya yajin aiki na gargaɗi

Ƙungiyar ƙwadago ta NLC a Najeriya ta sanar da aniyar shiga yajin aikin gargaɗi na kwana biyu a kan matsin rayuwa da ‘yan ƙasar ke ciki sakamakon janye tallafin fetur.
NLC ta ce za ta gudanar da yajin aikin ne a ranakun Talata da Laraba mai zuwa.
A ranar da aka rantsar da shi, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya janye tallafin man fetur, yanayin da ya haifar da tsadar litar man fetur a gidajen mai daga naira 197 zuwa 617.
NLC ta nuna ƙin amincewa da matakin gwamnati da aiwatar da zanga-zanga a faɗin ƙasar.
Shugaba Tinubu ya sha ganawa da ‘yan ƙwadagon a kokarin ganin an cimma daidaito.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai