Home » Kwamishinan ƴan sandan Kano ya gayyaci wasu da ke tunzura A.A. Rufa’i

Kwamishinan ƴan sandan Kano ya gayyaci wasu da ke tunzura A.A. Rufa’i

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Kwamishinan ƴan sandan Kano ya gayyaci wasu da ke tunzura A.A. Rufa'i

Kwamishinan ƴan sandan jahar Kano CP Muhammad Usaini Gumel ya bayar da umarnin gudanar da bincike kan masu amfani da rashin lafiyar A.A. Rufa’i wajen tunzura da yaɗa shi a safukan sada zumunta.

Wannan dai na zuwa bayan da lauyan A.A. Rufa’i da aka fi sani da Bill gate, Barista Badamasi Sulaiman Gandu, ya shigar da koken yadda wasu matasa ke amfani da shafukan sada zumunta suna ƙara tunzura shi da tsokanarsa har ma ya yi zargin cewa ana sanya masa ƙwaya a lemon kwalba dan ya sha ya ƙara tunzura shi.

Manema labarai sun rawaito cewa mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jahar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar da karɓar korafin da kuma umarnin da kwamishinan ƴan sandan jahar CP Muhammad Gumel ya bayar na gayyato wasu daga cikin mutanen da ake zargi dan faɗaɗa bincike kan zargin.

SP Kiyawa, ya ce rundunar ba za ta zura ido ba, wasu na aikata abubuwan da ba su dace ba, wanda ya zama wajibi a ɗauki mataki kan lamarin domin kowanne ɗan ƙasa yana da yanci da bai kamata a ci zarafinsa ba ta kowacce hanya.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?