Rundunar ‘yan sanda ta jihar Kano ta sanya tukuicin naira dubu ɗari uku ga duk wanda ya ba wa hukumar bayani game da wasu ‘yan daba da take nema ruwa a jallo.
Wannan na zuwa ne a wani ɓangare na cigaba da yaƙi da ayyukan daba da ƙwacen waya a jihar nan wanda kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano ya sha alwashin kawo ƙarshensa.
Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa. Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.