Home » Majalisun dokokin Najeriya na shirin fara nazari kan sunayen ministoci

Majalisun dokokin Najeriya na shirin fara nazari kan sunayen ministoci

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Majalisun dokokin Najeriya na shirin fara nazari kan sunayen ministoci da ke gabanta

A yau Laraba ne ake sa ran za a karanto sunayen mutanen da Shugaba Tinubu zai naɗa a matsayin ministoci a zauren majalisar dattawa, bayan an daɗe ana jira.

Hakan na zuwa ne bayan da shugaban ƙasar ya aike da jerin sunayen ga majalisar dattawa a jiya Talata, 18 ga watan Yuli,

Rahotanni sun nuna cewa magatakardan majalisar, Magaji Tambuwal ya karɓi wasiƙar shugaban ƙasar mai ɗauke da sunayen ministocin a jiya Talata.

Haka kuma Shugaban ƙasa Tinubu ya miƙa sunayen ministocin ga hukumomin tsaron farin kaya ta DSS da hukumar da ke yaki da masu yiwa tatttalin arzikin ƙasa zagon ƙasa ta EFCC domin yin binciken ƙwaƙwaf a kansu.

Wasu majiyoyi sun yi iƙirarin cewa hakan da shugaban ƙasar ya yi wata hanya ce ta tsame wasu manyan jiga-jigai waɗanda kai tsaye ba za a iya ƙin basu muƙamin minista ba.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?