Home » Mai Alfarma Sarkin Musulmi Ya Ayyana Juma’a a Matsayin Ranar Sallah Ƙarama

Mai Alfarma Sarkin Musulmi Ya Ayyana Juma’a a Matsayin Ranar Sallah Ƙarama

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Abubakar Sa’ad III ya sanar da ganin jinjirin watan Shawwal a Najeriya.

Sarkin Musulmi Alhaji Sa’ad Abubakar III ya ce ganin jinjirin watan da aka yi a a kasar ya sanya ranar Juma’a 21 ga watan Afrilu, 2023 ta zamo 1 ga watan Shawwal, 1444.

Kwamitin tantance ganin wata karkashin jagorancin Maigirma Wazirin Sakkwato Farfesa, Sambo Wali Junaidu ne ya jagoranci aikin tabbatar da ganin watan.

Domin haka Sarkin Musulmi ya tabbatar da gobe Juma’a a matsayin ranar sallah ƙarama

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?