Home » N-Power: Gwamnatin tarayya za ta biya bashin hakkokin ma’aikata

N-Power: Gwamnatin tarayya za ta biya bashin hakkokin ma’aikata

by Muhammad Auwal Suleiman
1 comment
N-Power: Gwamnatin tarayya za ta biya bashin hakkokin ma'aikata

Gwamnatin tarayya ta ba da tabbacin cewa za ta biya waɗanda ke bin bashin haƙƙoƙinsu da ke cikin shirin nan da aka dakatar na N-Power, da kuma ba a kai ga biyansu ba.

Ministar hukumar Jinƙai da Yaƙi da Fattara, Betta Edu,  ce ta bayyana hakan a jiya ta hannun shugaban kula da shirin na N-power ta ƙasa, Akindele Egbuwalo.

A ranar Asabar ne, ministar ta sanar da dakatar da shirin saboda wasu dalilai da suka gano ake yi da ba su dace ba.

Inda ta ce akwai buƙatar a yi bincike game yawan waɗanda suke cikin tsarin da, da waɗanda suka kammala, da waɗanda ake suke bin albashi, da kuma ko su ma’aikatan na zuwa wuraren ayyukansu ka ba sa zuwa.

Sannan ta ce akwai buƙatar a gudanar da bincike game da yadda ake kashe kuɗaɗen da ake warewa shirin na N-Power.

Inda ta buƙaci ‘yan Najeriya da su kalli wannan dakatarwar da idon basira tare da fahimtar dalilai da suka tilasta dakatar da shirin.

A ƙarshe, ta ba da tabbacin cewa da zarar an kammala tantance waɗanda ke bin bashin haƙƙoƙinsu.

You may also like

1 comment

Bala December 20, 2023 - 11:23 am

Bala zamfara gusau noma

Reply

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?