• Home  
  • Za mu samu Naira tiriliyan 1 daga noma ~Gwamnan Neja
- Labarai

Za mu samu Naira tiriliyan 1 daga noma ~Gwamnan Neja

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago ya ce gwamnatinsa tana sa ran samun  Naira tiriliyan ɗaya na kudin shiga da za a samu daga Kanfanin Samar da Abinci da Sufuri na Jihar a cikin shekaru biyar masu zuwa. Mashawarci na musamman ga gwamnan kan kafafen yaɗa labarai na zamani, Abdullberqy Ebbo, ne ya bayyana a hakan […]

BAGO

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago ya ce gwamnatinsa tana sa ran samun  Naira tiriliyan ɗaya na kudin shiga da za a samu daga Kanfanin Samar da Abinci da Sufuri na Jihar a cikin shekaru biyar masu zuwa.

Mashawarci na musamman ga gwamnan kan kafafen yaɗa labarai na zamani, Abdullberqy Ebbo, ne ya bayyana a hakan a ciki wata sanarwa da ya fitar a jiya a Abuja.

A cewarsa, wannan shiri da gwamnati ke yi, zai samar wa da  manoma dubu 100 aikin yi waɗanda ake sa ran za su noma kusan hekta dubu 100 a fadin jihar.

Ya ce tuni aka ƙulla yarjejeniya tsakanin shugaban kanfanin samar da abincin na jihar Neja, Sammy Adigun, da kuma babban daraktan kanfanin TGI, Sadik Kassim.

 

Kuma a ƙarƙashin yarjejeniyar, gwamnatin jihar da kuma kanfanin samar da abincin za su ɗauki alhakin noma, da girbi da sayar da abubuwan da za a noma da suka haɗa da shinkafa da waken suya da masara da riɗi  ga kanfanin na TGI.

 

Kuma za a tabbatar da an samar da sama da tan dubu ɗari shida na kayan amfanin goma a cikin tsawon shekarun biyar masu zuwa.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai