Home » Za mu samu Naira tiriliyan 1 daga noma ~Gwamnan Neja

Za mu samu Naira tiriliyan 1 daga noma ~Gwamnan Neja

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
BAGO

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago ya ce gwamnatinsa tana sa ran samun  Naira tiriliyan ɗaya na kudin shiga da za a samu daga Kanfanin Samar da Abinci da Sufuri na Jihar a cikin shekaru biyar masu zuwa.

Mashawarci na musamman ga gwamnan kan kafafen yaɗa labarai na zamani, Abdullberqy Ebbo, ne ya bayyana a hakan a ciki wata sanarwa da ya fitar a jiya a Abuja.

A cewarsa, wannan shiri da gwamnati ke yi, zai samar wa da  manoma dubu 100 aikin yi waɗanda ake sa ran za su noma kusan hekta dubu 100 a fadin jihar.

Ya ce tuni aka ƙulla yarjejeniya tsakanin shugaban kanfanin samar da abincin na jihar Neja, Sammy Adigun, da kuma babban daraktan kanfanin TGI, Sadik Kassim.

 

Kuma a ƙarƙashin yarjejeniyar, gwamnatin jihar da kuma kanfanin samar da abincin za su ɗauki alhakin noma, da girbi da sayar da abubuwan da za a noma da suka haɗa da shinkafa da waken suya da masara da riɗi  ga kanfanin na TGI.

 

Kuma za a tabbatar da an samar da sama da tan dubu ɗari shida na kayan amfanin goma a cikin tsawon shekarun biyar masu zuwa.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?