Home » Najeriya Sabon Jini Take Buƙata ~ Obasanjo

Najeriya Sabon Jini Take Buƙata ~ Obasanjo

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Obansanjo

Tsohon shugaban ya bayyana hakan a wurin wani taro a jihar Legas, inda ya koka da yadda rashin tsaro a ƙasar nan ke ci gaba da jefa mutane cikin fargaba da yunwa.

Domin magance wannan matsala, Obasanjo ya ce akwai buƙatar kyakkyawan jagoranci da ai inganta rayuwar al’umma.

Ya ce za a iya samar da kyakkyawan shugabanci ne kaɗai idan aka samu sabbin jagorori masu tsoron Allah da son kawo canji da kuma jin cewa al’umma za su bautawa.

Sannan ya ce duk yawan arziƙin da muke taƙama da shi ba zai kai mu ko’ina ba, idan aka ce babu kyakkawan shugabanci a ƙasar nan wanda ya ce hakan ne ya sa shugabanci ya zama muhimmin abun damuwa a Afirka.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?