Home » Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano Ta Kame Mutane 93 Bisa Zargin Ta da Tarzoma

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano Ta Kame Mutane 93 Bisa Zargin Ta da Tarzoma

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano Ta Kame Mutane 93 Bisa Zargin Ta da Tarzoma

‘Yan sandan jihar Kano sun bayyana kame mutane casa’in da uku cikin mako ɗaya da ake zargi da laifuka daban-daban.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, Muhammed Usaini Gumel ne ya bayyana haka a jiya a yayin wata zantawa da manema labarai.

Kwamishinan ya ce waɗanda aka kama ana zargin an ɗau hayarsu ne domin ta da zaune tsaye a yayin bikin rantsar da gwamnan Kano da kuma mataimakinsa.

Ya kuma bayyana cewa an samu waɗannan mutane da muggan makamai da kuma ta’ammali da makamai masu illar gaske da kuma yunƙurin amfani da makaman wajen gudanar da sace-sace da kuma kawo cikas ga rantsar da sabon gwamna da aka yi.

Kwamishinan ‘yan sandan ya tabbatar da cewa za a miƙa su ga kotu domin girbar abin da suka shuka da kuma zama izina ga ‘yan baya.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?