Home » Shugaba Buhari Ya Miƙa Ta’aziyyarsa Ga Alhaji Aminu Dantata

Shugaba Buhari Ya Miƙa Ta’aziyyarsa Ga Alhaji Aminu Dantata

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bayyana alhininsa game da rasuwar Hajiya Rabi Dantata, matar hamshakin dan kasuwa, mai taimakon jama’a a nan Jihar Kano, Alhaji Aminu Dantata.

Shugaban, ta bakin mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Malam Garba Shehu, a jiya, ya bayyana marigayiyar a matsayin mace mai tausayi da taimakon marasa galihu da kuma sha’awar hidimta wa mutane.

Ta kuma kasance mai farin jini mai son raba duk abin da take da shi ga al’umma.

Shugaban Buhari ya yi addu’ar Allah ya jiƙanta tare da karɓi ayyukanta na alheri, ya kuma bai wa iyalan Dantata hakurin jure wannan babban rashi da aka yi da ma al’ummar Musulmi bakiɗaya.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?