Shugaba Tinubu Ya Ayyana Sunayen Mutane 3 a Matsayin Hadimansa

Shugaba Tinubu Ya Ayyana Sunayen Mutane 3 a Matsayin Hadimansa

Zaɓaɓɓen shugaban ƙasar nan, Bola Ahmad Tinubu, ya ayyana sunanayen wasu mutane uku a matsayin masu taimaka masa cikin ƙunshin gwamnatinsa wacce ta fara a yau.

Mutanen da shugaban ƙasar ya naɗa sun haɗa da:

Ambasada Kunle Adeleke a matsayin cif-furotakwal na shugaban ƙasa.

Sai kuma tsohon kwamishinan labarai na jihar legas, Dele Alake, a matsayin mai Magana da yawun shugaban ƙasa.

Na ukun shi ne Olusegun Dada a matsayin mashawarci na musamman ga shugaban ƙasa kan kafafen sada zumunta na zamani.

Ana sa ran cewa shugaban ƙasar zai kammala naɗe-naɗensa ne cikin kwanaki 60 kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada wanda ya haɗa da muƙaman da ke buƙatar sahalewar majalisun ƙasar nan.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *