Home » Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu Zai Halarci Taron Kungiyar ECOWAS Karo Na 63

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu Zai Halarci Taron Kungiyar ECOWAS Karo Na 63

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu Zai Halarci Taron Kungiyar ECOWAS Karo Na 63

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu zai tafi kasar Guinea-Bissau domin halartar taron shugabannin kasashen kungiyar ECOWAS karo na 63.

Shugaban dai zai samu rakiyar wasu daga cikin manyan jami’an gwamnati kamar yadda sanarwar da mai magana da yawun sa, Dele Alake ta bayyana.

Taron da za a za a fara a gobe Lahadi, ana sa ran za a tattauna batutuwan da suka shafi yankin yammacin Afrika, musammanma rahoton zaman taro na 50 na kwamitin samar da zaman lafiya na kungiyar wanda ya kunshi kalubalen tsaro da kasashe mambobin kungiyar ke fuskanta.

Bayan nan akwai rahoton zaman taro na 90 na majalisar ministocin kungiyar ta ECOWAS kan harkokin kudi da aiwatar da kawusanci na bai daya a nahiyar Afirka da kuma rahoto kan halin da ake ciki a Mali da Burkina Faso da kuma Guinea.

Sauran abubuwan da ake saran tattaunawa a yayin taron, sun hada da shirin ECOWAS na samar da kudin bai daya da da dai sauran su.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?