• Home  
  • Tsohon Hadimin shugaba Buhari Ya Zama Mataimakin Shugaban Jaridar The Sun
- Labarai

Tsohon Hadimin shugaba Buhari Ya Zama Mataimakin Shugaban Jaridar The Sun

Tsohon Mai Ba Wa Shugaban Ƙasa Shawara a Kan Harkokin Yaɗa Labarai, Femi Adesina, ya ce, ya shirya karɓar mukamin mataimakin shugaban Jaridar The Sun, wanda ake sa ran zai fara aiki a ranar 1 ga watan Satumba.

Tsohon Hadimin shugaba Buhari Ya Samu Zama Mataimakin Shugaban Jaridar The Sun

Tsohon Mai Ba Wa Shugaban Ƙasa Shawara a Kan Harkokin Yaɗa Labarai, Femi Adesina, ya ce, ya shirya karɓar mukamin mataimakin shugaban Jaridar The Sun, wanda ake sa ran zai fara aiki a ranar 1 ga watan Satumba.

A baya dai Femi Adesina ya riƙe muƙamin Edita a Kamfanin Jridar ta The Sun, a matakai daban-daban.

Wannan bayani, ya fito ne daga bakin Adesinan a yayin da yake tattaunawa da manema labarai, Inda ya bayya na cewar, Shugaban Kamfanin, Senator Orji Kalu,  ya tabbatar da ba shi muƙamin.

Adesina ya ce a yayin da ya bayyana aniyarsa ta barin gidan jaridar a baya, Kalu ya shawarce shi a kan kada ya rubuta takardar barin aiki.

A maimakon haka sai ya ba shi damar ya je ya riƙe mukaminsa na Gwamnati, daga baya bayan ya gama, ya iya dawowa.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000