Home » UNICEF ta nuna shakunta game da shawo kan yawan bayan gida a sarari a Najeriya

UNICEF ta nuna shakunta game da shawo kan yawan bayan gida a sarari a Najeriya

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
UNICEF ta nuna shakunta game da shawo kan yawan bayan gida a sarari a Najeriya

Asusun Tallafawa wa Ƙananan Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya, UNICEF, ta ce da wahala Najeriya ta iya kawo ƙarshen matsalar bayan gida a sarari nan da shekarar 2025.

UNICEF ta ce jan ƙafar da ake wajen ɗaukar matakan da suka dace wajen cimma wannan muradi.

Jami’i na musamman da ke ofishin UNICEF  a Najeriya reshen jihar Legas, Monday Johnson, ne ya bayyana hakan a jiya a garin Ibadan a yayin wani taron kwana biyu da manema labarai na Kudu maso Yammacin ƙasar nan.

Ya ce jihar Jigawa ce kaɗai ta zama zakaran gwajin dafi da za a ce ba ta fama da matsalar yawan bayan gida a sarari.

Sannan ƙananan hukumomi 105 ne cikin 774 da ake da su a ƙasar nan, su ne aka tabbatar ba su da wannan matsala ta yawan bayan gida a sarari.

A cewarsa, idan aka cigaba da tafiya a yadda ake a yanzu, Najeriya za ta iya rabuwa da wannan matsala ne kaɗai nan da shekera ta 2046.

Ya kuma shawarci ‘yan jarida da su cigaba da wayar da kan al’umma kan illar yin bayan gida a sarari tare da samar da rahotanni na kawo mafita kan wannan matsala domin ƙarfafa wa gwamnati cigaba da ɗaukar matakan da suka dace.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?