Rahotanni daga shafukan sada zumunta na nuni da yadda al’ummar ƙasar nan suka wayi gari da farin cikin ganin Kanfanin MTN ya yafe wa kwatamominsa da yake bi bashin kuɗin kiran waya.
Wanann al’amari ya zo ne kamar a mafarki, inda da yawan mutane suka gaza ɓoye wannan jin daɗi tare da wallafa godiyarsu a shafukansu na sada zumunta da kuma WhatsApp.
Ba iya wannan ba wani rahoton ya nuna yadda wasu daga cikin mutane suka fara samun tallafin gwamnatin tarayya na Naira dub ashirin da biyar, 25,000, ta bankunansu.
Wanda shi ma a jihar Jigawa ta kai ga wasu sun garzaya kasuwa tare da siyo zabi domin gwangwaje wannan rana da farin ciki…