Home » Wasu Mahara sun kai hari gidan wani shugaba tare da halaka shi da ’ya’yansa 4

Wasu Mahara sun kai hari gidan wani shugaba tare da halaka shi da ’ya’yansa 4

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Wasu Mahara sun kai hari gidan wani shugaba tare da halaka shi da ’ya’yansa 4

Wasu Mahara sun kai hari gidan Ardon Birni da kewayen Zariya, Alhaji Shuaibu Mohammed inda suka halaka shi tare da ’ya’yansa guda 4 a daren Asabar.

Mai dakin marigayin, Mallama Halima Shu’aibu ta sanar da manema labarai cewa Maharan su 5 ne kuma sun fada masu gida ne da misalin karfe 10:00 na dare sannan suka tafi dakin Ardon inda suka kashe shi.

A cewarta daga nan ne sai suka bi daki-daki na ’ya’yan nasa su hudu, dukkansu magidanta, suka halaka su. Matar ta bayyana sunan ’ya’yan da aka kashe da suka hada da Adamu Shuaibu, Musa Shuaibu, Abubakar Shuaibu da kuma Haruna Ibrahim.

Halima ta kara da cewa bayan sun kammala kisan, sai kuma suka kora shanunsu kimanin guda 100. Shi ma da yake magana da manema labarai, daya daga cikin ’ya’yan Ardon da ya rage, Abdurrahman Shuaibu ya ce bayan sun gama da gidansu, maharan har ila yau sun kuma harbi mutane biyu a kan hanyarsu ta barin kauyen

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?