Home » Wata jami’a mai zaman kanta na shirin bai wa ‘yan asalin Kano gurbin karatu kyauta

Wata jami’a mai zaman kanta na shirin bai wa ‘yan asalin Kano gurbin karatu kyauta

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Wata jami’a mai zaman kanta na shirin bai wa ‘yan asalin Kano gurbin karatu kyauta

Mataimakiyar shugaban kula al’amuran daliban wata jami’a mai zaman kanta a kano ta bayyana cewa jami’ar na shirin zakulo hazikan dalibai ‘yan asalin Jihar, domin ba su gurbin karatu kyauta a matsayin gudummawa da karfafa gwiwa ga hazikan dalibai, domin tallafa wa kokarin gwamnatin Kano na bunkasa ilimi.

Jami’ar ta bayyana hakan ne a lokacin da take jawabi a wajen bikin baja kolin al’adun gargajiya da aka shirya wa sababbin daliban da aka rantsar domin fara sabon zangon karatu.

Ta ce wannan bikin al’adun ya shafi nuna sutura da yadda kabilu daban-daban da ke kasar har da tsarin rayuwarsu da shugabancinsu wanda ya hada da Fulani, Yaroba, Hausawa, Ebo da Barebari.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?