Home » Hadiza Gabon Ta Maka Wani Mutum A Kotu

Hadiza Gabon Ta Maka Wani Mutum A Kotu

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Wata ‘yar fim ta maka wani a kotu saboda ɓata mata suna

Shahararriyar ‘yar fim ɗin Kannywood, Hadiza Aliyu wacce aka fi sani da Hadiza Gabon ta maka wani mai suna Bala Musa a kotun majistare da ke kan hanyar Daura, a jihar Kaduna, inda take zarginsa da lafin ɓata suna.

Lauyan Hadiza Gabon, Mubarak Sani, ya bayyana cewa tauraruwar fim ɗin ta sha fama da baƙaƙen maganganu daga al’umma saboda zargin da wanda ta shigar ƙara ya yi kwanaki a kanta.
Ya ce da yawa daga cikin masu amfani da soshiyal midiya sun riƙa kiran wacce yake karewa a matsayin macuciya saboda ƙin auren Bala Musa da ta yi bayan karɓe masa kuɗi.

Lauyan ya ce wannan batu na karɓar kudin ƙarya ne.

Sai dai lauyan wanda aka maka a kotun, Naira Murtala, ya ƙi amsa laifin.

Nan take kuwa mai shari’a, Shamsudeen Sulaiman, ya tambayi ɓangaren da ke ƙarar ko suna da hujja da za ta tabbatar da wancan batu ƙarya ne kuma an ɓata wa wacce yake karewa suna.

Lauyan ya amsa da e, suna da shaida.

Daga nan mai shari’ar ya ba da belin wanda ake ƙarar bisa sharaɗin gabatar da mutane biyu waɗanda za su tsaya masa kuma wajibi su kasance mazauna jihar ta Kaduna kuma ma’aikatan gwamnati.

Sai mai shari’a ya ɗage sauraron ƙarar zuwa ranar 15 ga watan da muke ciki domin masu ƙara su gabatar wa da kotu da shaidunsu.

You may also like

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?