Home » Yanzu-yanzu: Kungiyar Ƙwadago Ta Janye Batun Shiga Yajin Aiki

Yanzu-yanzu: Kungiyar Ƙwadago Ta Janye Batun Shiga Yajin Aiki

Da ma dai a baya kungiyoyin ƙwadagon sun lashi takobin tafiya yajin aikin ne domin nuna nuna rashin amincewa da batun cire tallafin man fetur da gaza cika cika musu buƙatu bakwai da suka gundaya wa gwamnatin.

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
kungiyoyin ƙwadagon .

Kungiyoyi ƙwadago na NLC da TUC sun sanar da janye yajin aikin da suka yi niyyar faraea daga gobe.

Wannan na zuwa ne bayan wata tattaunawa ta gaggawa da kungiyoyin suna yi da ɓangaren gwamnatin tarayya a yau.

Da ma dai a baya kungiyoyin ƙwadagon sun lashi takobin tafiya yajin aikin ne domin nuna nuna rashin amincewa da batun cire tallafin man fetur da gaza cika cika musu buƙatu bakwai da suka gundaya wa gwamnatin.

Janye yajin aikin har’ila yau, wani yunƙuri ne na ba wa gwamnati damar cika alƙawuran da ta yi a yayin wannan zama.

Don haka, mataimakin shugaban ƙungiyar ƙwadago, kwamared Adeyanju, ya umarci dukkan ma’aikata da su koma bakin aiki daga gobe.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?