Home » Zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasar Najeriya Ya Dawo Daga Ziyarar da Ya Kai Faransa

Zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasar Najeriya Ya Dawo Daga Ziyarar da Ya Kai Faransa

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Zaɓaɓɓen shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya dawo ƙasar nan bayan wata ziyara da ya kai ƙasar Faransa inda ya shafe tsawon mako biyar.

A baya an bayyana cewa, dalilin tafiyar shi ne samun hutu bayan kammala yaƙin neman zaɓen da zaɓen da aka gudanar da ya tabbatar da shi a matsayin shugaban ƙasa mai jiran gado.

Tun farko an tsara cewa zaɓaɓɓen shugaban na Najeriya zai kwan biyu a Paris cikin ƙasar Faransa, daga nan kuma ya wuce zuwa birnin London, kafin ya dangana da ƙasar Saudiyya.

Sai dai rashin ganin sa a ƙasar Saudiyya lokacin aikin umrah, musamman daidai lokacin da shugaban ƙasar mai barin gado, Muhammadu Buhari yake can, ya haifar da jita-jita da raɗe-raɗi.

Tinubu ya sauka ne da yammacin a yau a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe, da ke Abuja babban birnin ƙasar nan.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?