Zababben Gwamnan Kano Ya Naɗa Sakataren Yada labaransa

Zababben Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da nadin Sanusi Bature Dawakin Tofa a matsayin sakataren yada labaransa zuwa lokacin karbar mulki.

A wata sanarwa da ya fitar da yammacin ranar Alhamis, mai dauke da sa hannun shugaban kwamitin karbar mulki, Abba Kabir Yusuf, ya bayyana Sanusi Bature a matsayin jajirttace kuma wanda yasan aikinsa.

Sanusi, wanda a baya ya yi aiki a bangarori da dama kama daga kungiyoyin cikin gida da na kasashen waje, shi ne mai magana da yawun kwamitin yakin neman zaben gwamna na jam’iyyar NNPP a zaben gwamna da aka kammala a jihar.

A ranar Laraba ne Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) a Jihar Kano ta bai wa zababben gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf takardar shaidar lashe zaben gwamnan da aka gudanar a ranar 18 ga wannan watan Maris.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *