PDP Ta Bugi Kirjin Cewa Ita Ce Za Ta Iya Dawo Da Najeriya Turba Mai Kyau.
Jam’iyyar PDP ta Najeriya ta ce babu gudu ba ja da baya kan shirye-shiryenta na gudanar da babban taronta wanda aka shirya yi a ranar 15 ga watan Nuwamban shekarar nan ta 2025 a jihar Oyo da ke kudancin Najeriya. PDP ta bayyana haka ne a wata sanarwa da ƙungiyar gwamnoninta ta fitar bayan taron […]