An Kama Hon Gudaji Kan Zargin Karɓar Kyautar Miliyan 70 Daga Emefiele
Rahotanni da yammacin Laraba sun ce hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC a Najeriya ta tsare tsohon ɗan majalisar tarayya mai wakiltar wani yanki a jihar Jigawa, wato Honarul Muhammad Gudaji Kazaure bisa zargin shi da aikata laifukan kuɗi.