Gwamnatin Kebbi ta ƙaryata rahoton mutuwar yara saboda yunwa
Gwamnatin jihar Kebbi da ke arewa maso yammacin Najeriya ta ce babu gaskiya a rahoton ƙungiyar likitoci ta Médecins Sans Frontières, MSF, kan mutuwar ƙananan yara sakamkon cutar tamowa a jihar. Wani rahoto da MSF ta fitar ya nuna damuwa kan ƙaruwar alƙaluman UNICEF da ke nuna cewa ana rasa kusan yara 30 cikin 100 […]