Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas
Majalisar zartaswar jihar Jigawa ta amince da fitar da naira biliyan 2.5 don nazarin yanayin kasa domin gano yuwuwar samun makamashin Uranium da ɗanyen mai da iskar gas a cikin jihar. Kwamishinan Yada Labarai, Matasa da Wasanni da Al’adu na Jihar, Hon. Sagir Musa ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema […]