An Hana Sanata Natasha Da Takwaranta Akpabio Ganawa Da ‘Yan Jarida
Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Abuja, a ranar Juma’a, ta haramta wa dakatacciyar sanatar Kogi ta tsakiya Natasha Akpoti-Uduaghan da Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya Godswill Akpabio yin hira da ‘yan jarida tun da ’yar majalisar ta shigar da ƙara kotu.