• Home  
  • Direba Ya Gudu Da Buhunan Masara 463
- Babban Labari - Labarai

Direba Ya Gudu Da Buhunan Masara 463

Ana zargin wani direban tirela ya gudu da buhunan masara 463 da aka aike shi da su, bayan da ya bai wa ɗan rakiyarsa guba a cikin shayi a yankin Maraban Jos da ke Jihar Kaduna. Wani ɗan kasuwa da ke safarar hatsi daga Jihar Kano zuwa kamfanoni a sassa daban-daban na Nijeriya, Injiniya Jamilu […]

Ana zargin wani direban tirela ya gudu da buhunan masara 463 da aka aike shi da su, bayan da ya bai wa ɗan rakiyarsa guba a cikin shayi a yankin Maraban Jos da ke Jihar Kaduna.

Wani ɗan kasuwa da ke safarar hatsi daga Jihar Kano zuwa kamfanoni a sassa daban-daban na Nijeriya, Injiniya Jamilu Haruna, ya shaida wa Aminiya cewa direban da ya ɗora wa masara buhu 463 domin kaiwa kamfanin Olam da ke Ilorin a Jihar Kwara, ya gudu da kayan.

“Kuɗin kayan sun kama Naira miliyan miliyan ashirin da ɗaya da dubu ɗari shida da tamanin da shida da ɗari huɗu.

“Wallahi jarin nawa ke nan ɗungurungum na dora a motar,” in ji ɗan kasuwar, wanda ya bayyana cewa direban ya ɗauko masa masarar ce a cikin tirela ƙirar Hoho mai taya 18 daga yankin Doguwa a Jihar Kano.

Ya ƙara da cewa direban ya sami nasarar guduwa da kayan ne bayan da ya ba wa mutumin da aka haɗa shi da shi a matsayin ɗan rakiya guba a shayi, sannan ya jefar da shi ya gudu da motar maƙare da kayan.

“Dukkanin buhunan 463 na masara da wobil ɗin kayan ya kwashe da su ya tsere. Wasu jami’an ’yan kamasho da suka saba sama mana motocin haya sun shiga cikin binciken. Haka nan ’yan sanda na ci gaba da gudanar da bincike don gano inda direban yake,” in ji ɗan kasuwar.

A zantawarsa da Aminiya, Injiniya Jamilu, ya ce tun bayan faruwar lamarin har yanzu ba a sami gano direban ba balantana kayan, lamarin da ya ce ya yi sanadiyyar raba shi da duk jarin da yake juyawa.

Yadda abin ya faru — Mai kaya

Ya ce, “Mukan yi safarar masara mu kai wa kamfanoni a Kano da ma maƙwabtan jihohi, wacce muke siye a kasuwannin yankin Doguwa da Tudun Wada a Kano da kuma Saminaka a Jihar Kaduna.

“A wasu lokutan idan kayan suka yi yawa a wasu sassan na Arewacin Nijeriya, mukan kai kaya har irin su jihohin Kwara da Oyo da ma Legas.

“Wannan karon na haɗa kaya buhu 463, sai na sa ’yan kamasho a Unguwar Bawa su kawo min mota. To su akwai hanyar da suke bi su tantance sahihancin direba kafin su haɗa mu da shi, don mu ba huruminmu ba ne.

“To a haka ne ’yan kamasho suka samo mana direba, muka yi cinikin kuɗin mota Naira miliyan ɗaya da dubu hamsin. Aka kawo min mota muka loda kaya a kan za a kai su Ilorin. Kuɗin kayan kuma sun kama Naira miliyan 21,640. Wallahi jarin nawa ke nan ɗungurungum na dora a motar,” in ji shi.

Ya ce sukan haɗa direban da aka ba su da amintaccen ɗan rakiya daga wajensu, “saboda gudun halin wasu direbobin na yi wa kayan da aka ɗora musu ɗauki ɗai-ɗai idan babu idon mai kaya ko wakilinsa.”

Injiniya Jamilu ya ce, “Direban da ɗan rakiyar sun tashi da kayan daga Doguwa suka kwana a Unguwar Bawa saboda dare ya yi, gari na wayewa suka shiga Marabar Jos a Kaduna, sai direban ya ce su tsaya su yi gyaran ƙafar motar saboda sun ɗan shiga ramuka.

“A nan ne ma direban ya kira ni ya ce akwai ragowar cikon kuɗinsa Naira 350,000, na tura masa N100,000 zai yi gyara, na tura masa kuma muka yi waya da ɗan rakiyata ya ce lafiya kalau,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa, “To tun wannan ranar ta 25 ga watan Yunin 2025 ban sake jin ɗuriyarsu ba. Na yi ta kiran yaron nawa da shi direban amma ba na samun su. Har gari ya waye ina kira ban samu ba, sai na ɗauka ko sun shiga wuraren da hanya babu kyau ne ko kuma babu sabis.

“Kawai sai ga ɗan sanda ƙashegari ya zo gidana ya ce akwai wani yarona da aka tsinta

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000