Karamar Ministar Harkokin Wajen Najeriya Mrs Bianca Odumegwu-Ojukwu ta jagoranci kulla sabuwar yarjejeniyar da kasar Israila domin yaki da ‘yan taadda da rashin tsaro a kasar.
Najeriya da kasar Isra’ila sun jaddada aniyarsu na zurfafa hadin gwiwa a muhimman fannoni da suka hada da yaki da ta’addanci, da bayanan sirri, da musayar bayanai, da kuma samar da kudade a fannin tsaro, da horar da jami’an tsaro a kasar.
- Shugaba Bola Tinubu Lafiyarsa Kalau – Gwamna Soludo
- Zaben Cike Gurbi: Jam’iyun Siyasa Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Zaman Lafiya A Kano
Wannan na kunshe a cikin wata sanarwar Karamar Ministar Harkokin Wajen Najeriya Mrs Bianca Odumegwu-Ojukwu, da takwararta ta Isra’ila, mataimakin ministan harkokin waje, Sharren Haskel-Harpaz suka sanya wa hannnu.
Sanarwar ta fito ne bayan wani babban taron da ya gudana a ranar Litinin din da ta gabata a Abuja.
wannan na kunshe a cikin wani labari da jaridar business day ta wallafa.

