• Home  
  • Gwamnatin Kamaru Ta Tabbatar Da Mutuwar Mutane 4 A Zanga-zangar Da Ake Ci Gaba Da Yi.
- Babban Labari - Labarai

Gwamnatin Kamaru Ta Tabbatar Da Mutuwar Mutane 4 A Zanga-zangar Da Ake Ci Gaba Da Yi.

Gwamnatin Kamaru ta tabbatar da cewa mutum hudu suka mutu a zanga-zangar da ƴanƙasar suka gudanar a ranar Lahadi a birnin Doula gabanin sanar da sakamakon zaɓen shugaban ƙasa a yau Litinin. Ɗaruruwan magoya bayan ɗantakarar adawa, Issa Tchiroma Bakari ne suka fito zanga-zangar. Hukumomi sun ce an kai wa ƴansanda da jami’an tsaro hari […]

Gwamnatin Kamaru ta tabbatar da cewa mutum hudu suka mutu a zanga-zangar da ƴanƙasar suka gudanar a ranar Lahadi a birnin Doula gabanin sanar da sakamakon zaɓen shugaban ƙasa a yau Litinin.

Ɗaruruwan magoya bayan ɗantakarar adawa, Issa Tchiroma Bakari ne suka fito zanga-zangar.

Tchiroma Bakary ya ƙalubalanci shugaba Paul Biya – wanda ya shafe shekara 43 yana shugabanci a ƙasar.

Tuni jagoran adawar ya ayyana cewa shi ne ya yi nasara a zaɓen, duk da cewa a yau Litinin ne ake sa ran sanar da sakamakon a hukumance.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000