• Home  
  • Shugaba Buhari Ya Ƙaddamar da Aikin Haƙar Man Fetur a Jihar Nassarawa
- Labarai

Shugaba Buhari Ya Ƙaddamar da Aikin Haƙar Man Fetur a Jihar Nassarawa

Shugaba Buhari Ya Ƙaddamar da Aikin Haƙar Man Fetur a Jihar Nassarawa

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ƙaddamar da aikin haƙar rijiyar man fetur a ƙaramar hukumar Obi a jihar Nasarawa da ke Arewa ta tsakiyar ƙasar.

Ƙaddamar da aikin tona rijiyar zai sa kamfanin mai na ƙasar NNPC, ya fara tono man fetur daga jihar.

A cikin watan Nuwamban bara ne dai shugaban ƙasar Muhammadu Buhari ya ƙaddamar da aikin haƙo man fetur a yankin Kolmani da ke tsakanin jihohin Bauchi da Gombe a yankin Arewa maso gabashin ƙasar.

Yawancin man da ƙasar ke da shi dai tana haƙoshi ne daga yankin Niger Delta a kudu maso kudancin ƙasar.

Najeriya dai ta dogara ne da man fetur da take fitarwa a matsayin hanayar samun kuɗin shiga,

Duk kuwa da ƙoƙarin da gwamnatocin ƙasar ke yi na faɗaɗa hanyoyin samun kuɗin shiga ga ƙasar.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai