Home » Adamawa: INEC Ta Dakatar da Tattara Sakamakon Zaɓen Bisa Karya Doka

Adamawa: INEC Ta Dakatar da Tattara Sakamakon Zaɓen Bisa Karya Doka

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Hukumar zabe mai zaman kantan ta kasa ta ta soke sakamakon zaben jahar adamawa tare da gayyatar kwamishinan zaben jahar da kuma wadanda abun yashafa zuwa babban ofishin hukumar dake birnin tarrayya Abuja

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa ta lura da da wata sanarwa da kwamishinan zaɓeN na jihar Adamawa ya yi wadda ya bayyana sakamakon zaɓen jihar duk da cewa ana kan tattara sakamakon.
Bayyana sakamako zaben yayin da ake tattara sakamako ya saɓa wa tsarin dokar hukumar, kuma ta bai wa baturen zaɓe damar bayyana sakamakon zaɓe ba kwamishinan zaɓe ba.
Wannan ya sa Hukumar zaɓen ta ƙasa ta dakatar da tattara sakamakon zaɓen tare da umartar hukumomi a jihar kan su gaggauta zuwa babban birnin tarayya a Abuja.
Wannan umarni ya fito ne daga bakin jami’in Labarai da Wayar da Kan Al’mma na Hukumar ta ƙasa,  Festus Okoye.
Sannan hukumar ta yi alƙawarin fitar da cikakken bayani a kan wannan al’amari.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?