Shugaban Ƙungiyar Manoma ta Ƙasa na Karamar Hukumar Kiyawa jihar Jigawa ya shiga hannu, kan badaƙalar kayan noman da Gwamnatin Tarayya ta ba wa manoma a farashi mai rahusa.
Da yake bayyana cewa za su fuskanci fushin doka ya bayyana takaici bisa yadda almundahanar ta dabaibaye shirin Gwamnatin Tarayya na bunƙasa noma da tallafa wa manoma da kayan noma a jihar.
A yayin da gwamnan yake rangadi a cibiyoyin rabon kayan noma a jihar ne ya bankaɗo yadda dillalai da jim’an gwmanati suke zagon ƙasa ga shirin.
Gwamnan ya ce, “Dillalai na zagon ƙasa ga wannan shiri, wanda hakan ke kawo wa manoma matsala wajen ci gaba da noma su. Ba za mu lamunci hakan ba,” in ji gwamnan.
Ba Za Mu Ragawa Tinubu A 2027 Ba-Atiku
Ya bayyana cewa “gwmanati ta sanya N159,187 a matsayin kuɗin kayan noman, wanda ta rage rabin kuɗinsa ga manoma
“Amma mun samu bayanai cewa ’yan kasuwa na ƙara musu N5,000 zuwa N10,000, wanda ƙarin nauyi ne ga manoma.
“Wannan zagon ƙasa ne ga ƙoƙarin gwamnati na tallafa wa harkar noma da manoma. Don haka za mu tabbatar an ƙwato duk haramtattun kuɗaɗen da aka karɓa a hannun manoma, a mayar musu,” a cewar Gwamna Namad