Firaiministan Pakistan, Shehbaz Sharif ya ce yunƙurin warware rikicin Amurka da Iran na ci gaba.
Wannan na zuwa ne bayan tattaunawa tsakanin ƙasashen guda biyu da aka gudanar a babban birnin Pakistan, Islamad a ƙarshen mako, ba ta cimma komai ba.
“Tsagaita wutar na ci gaba a daida lokacin da nake maganar nan, ana kuma yunƙurin samar da mafiya dangane da sauran batutuwan da ake taƙaddama a kansu, kamar yadda Sheriff ya shaida wa majalisarsa.

