An fara zanga-zanga a Abuja, babban birnin tarayya, yayin da jam’iyyun adawa da ƙungiyoyin farar hula da ƙungiyoyin kwadago ke zargin Majalisar Tarayya da tauye dimokuraɗiyya ta hanyar ƙin amincewa da ƙudirin da zai wajabta tura sakamakon zaɓe ta na’ura.
Zanga-zangar ta ɓarke ne bayan da ‘yan majalisa suka ƙi amincewa da wani sashe na gyaran Dokar Zaɓe da zai tilasta tura sakamakon zaɓe daga rumfunan kaɗa ƙuri’a zuwa wata cibiyar bayanai da jama’a za su iya gani.
Masu sukar matakin sun ce hakan na rage gaskiya da sahihanci a zaɓuka, tare da dawo da fargabar maguɗin zaɓe.
Ƙungiyoyi da dama sun bayyana shawarar a matsayin cin amanar amincewar jama’a.
Masu zanga-zangar sun fara taruwa a kusa da harabar Majalisar Tarayya a Abuja, yayin da ake fargabar cewa gangamin na iya yaɗuwa zuwa wasu jihohin ƙasar.
Ƙungiyoyin farar hula da masu goyon bayan jam’iyyun adawa na cewa wajabta tura sakamakon zaɓe ta lantarki muhimmin mataki ne wajen kare ƙuri’ar jama’a a ƙasar da ake yawan samun ce-ce-ku-ce kan zaɓe.
Kungiyar Kwadago ta Najeriya, NLC, ta gargaɗi cewa ƙin saka tanadin tura sakamakon zaɓe ta na’ura a doka na iya janyo zanga-zangar ƙasa baki ɗaya da ƙara rashin amincewar jama’a da tsarin zaɓe.
A halin da ake ciki, Majalisar Dattawan Najeriya ta sanar da kiran zaman gaggawa a ranar Talata, 10 ga Fabrairu, a lokacin da take fuskantar matsin lamba daga jama’a da kuma suka kan yadda ake gudanar da gyaran Dokar Zaɓe.
